Ana zanga-zangar neman Goodluck ya sake fitowa takarar Shugaban kasa

Date:

Daga Halima M Abubakar

Ɗaruruwan magoya baya, da su ka haɗa da matasa da gungun mata ne a yau Juma’a su ka yi tsinke a ofishin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Ebele Jonathan.

Magoya bayan, wandanda su ka cika ofishin nasa ɗauke da kwalaye masu ɗauke da sakonni daban-daban, sun yi kira a gare shi da ya fito takarar shugabancin ƙasa a 2023.

Tun misalin ƙarfe 8 na safe ne dai magoya bayan su ka isa ofishin na Jonathan ɗauke da kayan kida, inda su ke ta rera wakoki na goyon baya iri-iri.

Sun nuna takaicin su cewa tun da Jonathan ya bar mulki, yunwa, talauci, rashin tsaro da rashin aikin yi sun yi wa ƙasar katutu.

Masoyan na Jonathan sun ce al’ummar ƙasa, maza da mata sun zama almajirai sabo da irin tsauraran manufofin gwamnti mai ci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...