Ganduje zai siyawa Katsina United sabuwar mota

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Gwamnan Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana rashin jin dadinsa akan abinda ya faru a yayin wasan Kano Pillars da Katsina United a filin wasa na Sani Abacha dake kofar mata a Kano, musamman yadda wasu suka farfasa motar Katsina United da kuma tada hargitsi.

Hakan na kunshe ne cikin sanarwar da Babban sakataren yada labaran Gwamnan Malam Abba Anwar, ya aikowa Kadaura24 a yau dinnan.

Sanarwar  Ganduje yace za’a kafa kwamiti mai karfi, kuma za’a samar da sabuwar Mota ga Katsina United, domin mutanen Kano da Katsina duk daya ne, kuma zasu cigaba da kasancewa daya har abada.

Ganduje ya bukaci magoya bayan Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillers zasu daina daukar irin wannnan mumnunan mataki da zai zubar da kimar Jihar kano a idanun duniya.

Idan za’a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito magoya bayan Kano Pillers sun fasa motar yan wasan Katsina United bayan Wani wasa da Suka gudanar a filin wasa na sani abacha dake nan Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...