2023: Ganduje ya gargadi yan Siyasa kan yawo da makamai

Date:

Daga Rumaisa Lawan

Gwamnan Jihar kano Abdullahi Umar Ganduje ya ja kunne Yan Siyasa a Jihar nan da su guji Amfani da makamai a wuraren tarukan Siyasa.

Kadaura24 ta rawaito Gwamnan ya bayyana hakan ne yayi da ya jagoranci Kaddamar da Sabbin zababbun Shugabannin jam’iyyar APC na shiyyar Kano ta arewa Wanda ya gudana a Karamar Hukumar Bichi .
Gwamna Ganduje yace Amfani da makamai a wuraren tarukan Siyasa Bai dace da ga yan Siyasa masu manufa ba, Waɗanda kamata yayi su mai da hankali wajen inganta Rayuwar al’ummar su ba lalata Rayuwar Matasa ba.
Yace Jam’iyyar APC a Kano bata da burin da ya wuce inganta Rayuwar al’umma Musamman Mata da matasa domin su ne kashin bayan cigaban kowacce irin al’umma.
Gwamna Ganduje ya Kuma bukaci sabbin Shugabannin jam’iyyar dasu Mai da hankali wajen shiga lungu da sako na yankinsu don su wayar musu da Kai, su fahimci aiyukan alkhairi da jam’iyyar ta Gudanar tsahon Shekaru 8 da suka gabata a Kasar nan.
Wakilinmu ya rawaito mana cewa taron ya sami halartar ‘ya’yan jam’iyyar daga Kananan Hukumomi goma Sha uku dake yankin kano ta arewa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...