Buhari, El-Rufai, KADCCIMA sun karrama Dangote a kasuwar baje koli

Date:

Madina Salisu Dukawa
 Shugaban kasa Muhammadu Buhari da mai masaukin baki Gwamnan jihar Kaduna sun yabawa shugaban Rukunin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, bisa kwarin gwuiwar sa wajen habbaka Kasuwanci da kuma taimakawa al’ummar kasar nan.
 Mutanen biyu sun bayyana hakan ne a wajen bikin baje kolin na Kaduna karo na 43 wanda shugaban kasar ya Kaddamar a karshen mako.
 Wadanda suka shirya bikin baje kolin cibiyar Kasuwanci,ma’adinai da noma ta jihar Kaduna wato (KADCCIMA) ya kuma bayyana Dangote a matsayin wanda ya fi bayar da gudunmowa ga cigaban tattalin arziki da Kuma gudanar da aiyukan Jin kai ga al’umma ta karkashin Gidauniya Aliko Dangote.
 Shugaba Buhari, wanda ya samu wakilcin Ministan Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Otunba Niyi Adebayo, ya kuma ziyarci rumfar Dangote inda ya ce kasar nan na godiya da irin tallafin da rukunin Kamfanoni Dangote ke baiwa al’ummar Nigeria.
 Ya bayyana Aliko Dangote a matsayin abokinsa saboda irin gudunmawar da yake bayarwa ga tattalin arzikin Najeriya, tallafawa ayyukan gwamnati da na zamantakewa.
 Kamfanin Dangote shi ne mafi girma wajen daukar nauyin Kasuwar baje kolin ta kasa da kasa a Kaduna karo na 43 da a yanzu haka ta ke gudana mai taken: Sake damarar bunkasa tattalin arzikin Najeriya don yayi dai-dai dana sauka kasashen duniya.
 A Jawabinsa gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufia, ya ce gwamnatin jihar Kaduna na samar da yanayin da masu zuba jari masu zaman kansu kamar su Dangote za su je jihar Kaduna don zuba jari.
 Kamfanin Dangote ne ke da hannun jari mafi girma a Kamfanin Mota na Dangote Peugeot da ke Kaduna.
 Gwamnan wanda ya samu wakilcin kwamishinan kasuwanci, kirkira da fasaha, Farfesa Kabiru Mato, ya ce jihar ta samar da tsare-tsare na sada zumunta domin jawo hankalin masu zuba jari na gida da waje.
 Da yake jawabi a wajen bikin bude taron, Darakta Janar Usman Saulawa ya yaba da alakar da ke tsakanin rukunin Dangote da cibiyar KADCCIMA.
 “Rukunin Dangote alama ce ta duniya a duniyar kasuwanci da masana’antu hakanan zan iya  ƙarawa da cewa kowanne gida ana amfani da kayan Dangote, Sannan kuma an san Dangote da ayyukan jin kai ta karkashin gidauniyar Dangote,” inji shi.
 Ya ce kamfanoni daga Indiya, Pakistan, Morocco, Chadi, Senegal, Mali, Jamhuriyar Nijar da kuma Bangladesh suna halartar bikin baje kolin kasuwanci.
 Kamfanonin da ke halartar taron a karkashin masana’antun Dangote sun hada da Dangote Cement, Dangote Sugar, NASCON, da Dangote Taki.
 Sanarwar da Sashen Sadarwa na Kamfanin na Kamfanin Dangote ya fitar ta ce mahalarta taron da ke neman yin kasuwanci da duk wani reshen kamfanin na iya cin gajiyar irin wannan damar ta wani tsari na musamman a rumfar.
 Ta bayyana jihar Kaduna a matsayin daya daga cikin manyan jihohin da ake Amfani da kayan Kamfanin a kasar nan, idan aka yi la’akari da matsayinta na tarihi a matsayin hedkwatar siyasar Arewacin Najeriya.
 Ta ce sabon takin Dangote da ya zama abun so ga manoma za a iya Samun shi a rumfar Kamfani.
 Sanarwar ta kara da cewa, baya ga kayayyakin da ake siyar da su a kan farashi mai sauki tare da fakiti na musamman, ana kuma gabatar da kayayyakin kyaututtuka ga kwastomomi a rumfar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...