Yahaya Bello ya Amince da biyan mafi karanci albashi na naira dubu 30 ga Ma’aikatan Jihar kogi

Date:

Gwamnatin Jihar Kogi karkashin jagorancin Gwamnan Yahaya Bello ta amince da aiwatar da biyan ma’aikatan Jihar sabon tsarin albashi na naira dubu talatin.

Sakataren gwamnatin Jihar Mrs Folashade Arike-Ayoade, ce ta sanar da haka bayan ganawa da kungiyar kwadago a garin Lokoja.

Daily News24 ta rawaito Mrs Folashade ta kara dacewa tun farko an sami jinkiri ne wajen aiwatar da sabon tsarin albashin sakamakon rashin ganawar da kwamatin da aka kafa kan tsarin albashin bayayi akai-akai, a sabila da annobar korona.

Dayake jawabi mataimakin gwamnan jihar Chief Edward Onoja, yace abun farinciki ne ace gwamnati ta fara biyan ma’aikata mafi kankantar albashi na naira dubu talatin, inda ya yabawa kungiyar kwadago reshen jihar bisa dattakun da ta nuna batareda sun kai ruwa rana ko tafiya yajin aiki ba.

Shima anasa jawabin shugaban kungiyar kwadago ta kasa reshen jihar Mr Onuh Edoka,” yace munji dadi abinda gwamna Yahya Bello yayi, dafari har mun sanar zamu shiga yajin aiki, amma yanzu mun dakatar da wannan batu saboda gwamnati tayi abinda ya kamata tayi’’.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...