Wanda ake zargi da kisan Hanifa Abubakar ya ce bashi ya kwashe ta ba

Date:

A zaman kotun na yau Litinin karkashin  mai shari’a Usman Na’abba, Abdulmalik Tanko ya ce kokadan ba shi ya kashe Hanifa Abubakar ba kuma bashi da masaniya kan aikata kisan.

Kadaura24 ta rawaito bayan da aka gurfanar da shi a gaban babbar kotun jiha ranar litinin wanda ake zargin ya ce ya yarda ya sace ta amma bashi ya kashe ta ba.

Idan za a iya tunawa dai a baya Abdulmalik Cikin Wani faifen video da Jami’in hulda da Jama’a na yan sandan Jihar Kano ya wallafa a Shafin Facebook, ya amsa kisan Hanifa bayan da rundunar ‘yan sanda ta yi holinsa a shalkwatarsu.

Har ma ya bayyana cewar ya kasheta ne da shinkafar bera ta N100 bayan da ya saceta ya kuma boyeta a wani wuri.

Wannan ce ta sanya alkalin kotun ya dage shari’ar har zuwa ranar 2 da 3 ga Maris mai kamawa domin sauraron karar, ya kuma bayar da umarnin a ci gaba da tsareshi a gidan yari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...