Gwamna Ganduje ya umarci hukumomin tsaro da su bankado wadanda suka kashe Rukayya Mustapha

Date:

Daga Zakariyya Adam Jigirya
 Gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bukaci jami’an tsaro da su gaggauta bankado wadanda suka kashe Rukayya Mustapha, matar aure da wasu ‘yan bindiga suka kashe a unguwar Danbare dake nan Kano.
 Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a lokacin da yake jajantawa iyalan mamaciyar a unguwar Dorayi dake karamar hukumar Kumbotso a jihar.
 Cikin Wata sanarwa da Babban Sakataren yada labaran Mataimakin Gwamna Hassan Musa fagge ya aikowa Kadaura24 yace wanda ya samu wakilcin mataimakinsa Dakta Nasiru Yusuf Gawuna ya ce gwamnatinsa ta dukufa wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Kano.
 ” cikin tsananin kaduwa muka samu labarin rasuwar Marigayiya Rukayya Mustapha… Ina mai tabbatar muku da cewa ba za mu bar wani abu haka kawai ba, dole sai an nemo Waɗanda Suka aikata Wannan mummunan aiki”. Inji Ganduje
 “A madadin gwamnati da al’ummar jihar ina Allah wadai da wannan aika-aika tare da addu’ar Allah ya jikan ta yasa tana Jannatul Firdaus tare da baiwa ‘yan uwanta hakurin  jure rashin”. Ganduje ya ce”.
 A nasa bangaren, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Sama’ila Shu’aibu Dikko ya bayyana cewa kawo yanzu an kama mutane 5 da ake zargi, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike domin zakulo wadanda suka kashe matar .
 Ya kuma yi nuni da cewa, wadanda suka yi ta’ammali da miyagun kwayoyi ne suke aikata irin wadannan laifuffuka, shi ya sa suke kama duk wadanda suke yi safarar miyagun kwayoyi domin dakile sake afkuwar lamarin.
 Dikko ya kuma bayar da tabbacin cewa, hukumomin tsaro za su rubanya kokarinsu na ganin ba’a sake Samun Faruwar irin  wadannan laifuka ba nan gaba.
 Tawagar ta kunshi kwamishinoni, Daraktan DSS Alhassan Muhammed da shugaban karamar hukumar Kumbotso Hassan Garban Kauye.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...