Turawa da larabawa sama da 200 ne Buhari ya Amince su zama yan Nigeria, bayan sun nema

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida
Majalisar Zattarwa ta kasa ta amince da baiwa mutane dari biyu da tamanin da shida yan kasashen waje takardar izinin zama yan Najeriya.
KADAURA24 ta rawaito Ministan harkokin Gidan Rauf Aregbesola ne ya sanar da haka ga manema labaran Fadar Shugaban Kasa, bayan kammala zaman Majalisar Zartarwar ta Kasa na Wannan makon a Fadan shugaban kasa.
Yace akwai Mutane da dama yan kasashen waje Waɗanda suke sha’awar Zama Yan Nigeria, Kuma Muna binsu Muna tsantsancewa don gudun kada a yi kitso da kwarkwata”.
Ministan yace daga Cikin Waɗanda suka halacci tantancewa da akai Musu domin Zama cikakkun Yan Nigeria sun fito ne daga kasashen Amuruka da Australia da yan kasashen larabawa da dai Sauransu.
” Daga Cikin Waɗanda muka tantance mun Sami Mutane dari biyu da tamanin da shida (286)  Waɗanda Suka chanchanci Gwamnati ta basu shaidar Zaman cikakkun Yan Nigeria”. Inji Ministan
Rauf Aregbisola yace Wannan Wani Abu ne da ya kamata ‘yan Nigeria su Maida hankali wajen Gina Kasar, Inda yace Yayin da Wasu daga cikin Mutanen Kasar nan suke komawa Zuwa Wasu kasashen, sai gashi Wasu daga kasashe daban-daban Suna son su zama Yan Nigeria.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

  Jam’iyyar NNPP ta nemi afuwar Shugaban kasa Bola Tinubu...

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...