Turawa da larabawa sama da 200 ne Buhari ya Amince su zama yan Nigeria, bayan sun nema

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida
Majalisar Zattarwa ta kasa ta amince da baiwa mutane dari biyu da tamanin da shida yan kasashen waje takardar izinin zama yan Najeriya.
KADAURA24 ta rawaito Ministan harkokin Gidan Rauf Aregbesola ne ya sanar da haka ga manema labaran Fadar Shugaban Kasa, bayan kammala zaman Majalisar Zartarwar ta Kasa na Wannan makon a Fadan shugaban kasa.
Yace akwai Mutane da dama yan kasashen waje Waɗanda suke sha’awar Zama Yan Nigeria, Kuma Muna binsu Muna tsantsancewa don gudun kada a yi kitso da kwarkwata”.
Ministan yace daga Cikin Waɗanda suka halacci tantancewa da akai Musu domin Zama cikakkun Yan Nigeria sun fito ne daga kasashen Amuruka da Australia da yan kasashen larabawa da dai Sauransu.
” Daga Cikin Waɗanda muka tantance mun Sami Mutane dari biyu da tamanin da shida (286)  Waɗanda Suka chanchanci Gwamnati ta basu shaidar Zaman cikakkun Yan Nigeria”. Inji Ministan
Rauf Aregbisola yace Wannan Wani Abu ne da ya kamata ‘yan Nigeria su Maida hankali wajen Gina Kasar, Inda yace Yayin da Wasu daga cikin Mutanen Kasar nan suke komawa Zuwa Wasu kasashen, sai gashi Wasu daga kasashe daban-daban Suna son su zama Yan Nigeria.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...