Uwar jam’iyyar APC ta bayyana dalilin da yasa ba ta rantsar da shugabannin jam’iyyar na kano ba

Date:

Daga Halima M Abubakar

Uwar Jam’iyar APC ta Ƙasa ta bayyana dalilin da ya sanya ba ta rantsar da shugabannin jam’iyar na Jihar Kano ba.

Kadaura24 ta rawaito cewa a ranar Alhamis da ta gabata ne dai jam’iyar ta rantsar da shugabannin jam’iya na jiha a jihohi 34 amma banda Kano da Sokoto.

Da ya ke bayani a kan dalilan da ya sanya ba a rantsar da shugabannin jam’iya na Kano ba a jiya Juma’a a Abuja, Sakataren Kwamitin Riƙo na APC na Ƙasa, John Akpanudoedehe, ya ce babu wani abin damuwa a kan matakin.

A cewar sa, uwar jam’iyar ta ɗauki matakin dakatar da rantsar da shugabannin jam’iya na Kano ne domin amfanin ƴan jam’iyar, jihar da kuma ƙasa baki ɗaya.

Ya ce APC na son zaman lafiya kuma Kano ta zama kamar nan ne Shalkwatar jam’iyar, inda ya ce ba za a yi wani abu da zai kawo naƙasu ga zaman lafiyar jam’iyar a jihar ba.

Daily Nigerian ta rawaito Akpanudoedehe ya ƙara da cewa akwai maganar shari’ar jam’iyar a kotu, sabo da haka uwar jam’iyar taki yin abun da zai zama kuskure a gareta ba Saboda lamarin na gaban kotu.

Sai dai kuma Akpanudoedehe bai fadi dalilin da ya sa jam’iyar ba ta rantsar da shugabannin jam’iya na Sokoto ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...