Yanzu Yanzu: APC ta sake kiran Ganduje da Shekarau taron gaggawa

Date:

Daga Zakariyya Adam Jigirya
 Shugaban kwamitin rikon jam’iyyar APC Mai Mala Buni, ya sake kira taron gaggawa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC na Kano.
 Wadanda aka gayyata taron sun hada da Gwamna Abdullahi Ganduje da Sanata Ibrahim Shekarau da wasu fitattun masu ruwa da tsaki daga ko wane bangare na bangarorin biyu.
Kadaura24 ta rawaito a taron na ranar Juma’a, bangarorin biyu sun gabatar da buƙatunsu a gaban shugabannin jam’iyyar na Kasa yayin Zaman sulhun.
 Wasu majiyoyin daga wajen taron sun ce gwamnan ba ya son baiwa tsagin Shekaru Manyan mukamai a  jam’iyyar, Amma dai ya bukaci su Shekarau su bada sunayen wadanda suke so domin ya basu mukamai a gwamnatinsa.
 APC ta Kano ta Sami kanta a wannan ne sakamakon rikicin da ya barke tsakanin bangaren Gwamna Ganduje da bangaren Malam Shekarau.
 Rikicin dai ya kai ga gudanar da gudanar da zaben Mazabu dana kananan hukumomi da na jiha, inda Abdullahi Abbas ya zama shugaban jam’iyyar na jiha tsagin Ganduje da Ahmadu Danzago daga tsagin Malam Shekarau.
 Jaridar DAILY NIGERIAN ta ruwaito cewa, Dan Majalisa mai wakiltar karamar hukumar birni, Shaaban Sharada Shi ne yake daukar nauyin duk Wannan shari’u da zabukan da tsagin Shekarau sukai.
 A halin yanzu dai ana gudanar da taron ne a masaukin Gwamnan Yobe dake Asokoro Abuja.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...