Kotu ta bayar da belin Muaz Magaji Dan Sarauniya bisa wasu sharudda

Date:

Wata kotu a Jihar Kano da ta bayar da belin tsohon kwamishinan ayyuka na jihar, Injiniya Mu’azu Magaji Dan Sarauniya.

Kotun mai lamba 58 da ke zamanta a unguwar Nomansland ta bayar da belin ne kan naira miliyan daya, tare da gindaya masa wasu sharuda da sai ya cika belin zai bayu.

BBC Hausa ta rawaito mai shari’a Aminu Gabari ya ce bayan biyan kudin da Dan Sarauniya zai yi sai ya kuma ajiye fasfo dinsa na tafiya.

Kazalika zai kawo mutum biyu da za su tsaya masa, dole na farko ya zama mai garin kauyen Sarauniya wato kauyen da ya fito, na biyun kuma dole ya zama limamin garinsu ko kuma kwamandan Hizban garin.

A ranar 27 ga watan Janairun da ya gabata ne ‘yan sanda suka kama Injiniya Mu’azu a Abuja babban birnin Najeriya.

An kuma mayar da shi jihar Kano inda ‘yan sanda suka gabatar masa da tuhume-tuhumen da ake zarginsa da su, na keta mutunci gwamnan Jihar Abdullahi Umar Ganduje

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...