SERAP ta kai karar Buhari kotu kan batan Naira biliyan 3

Date:

Daga Halima M Sadeeq

Kungiyar SERAP mai fafutukar yaki da cin hanci a Najeriya ta shigar da karar Shugaba Buhari gaban kotu “kan gaza gudanar da bincike game da zargin da ake yi na batan kudaden da suka kai naira biliyan 3 daga ma’aikatar kuɗi ta kasar, domin tabbatar da an gurfanar da wadanda ake zargi da hannu ciki da kuma kwato kudaden.”

Karar ta biyo bayan batan dabon da ake zargin da ofishin babban akanta janar na kasar ya shigar a 2018 da 2019 na rahoton da yake fitarwa, wanda aka batar da su ba bisa ka’ida ba ko kuma ba a bayar da bayanansu ba.

Sakon taya Murnar Samun shugabancin jam’iyyar SDP a Jihar Kano

BBC Hausa ta rawaito karar mai lamba FHC/L/CS/148/22 an shigar da ita ne a ranar Juma’ar da ta gabata a wata babbar kotun Tarayya da ke Lagos, kamar yadda SERAP ta bukata:

“umarnin da zai sanya Shugaba Buhari ya tabbatar da an gudanar da bincike game da zargin da ake yi na batan naira biliyan 3.1 wadanda kudaden mutanen Najeriya ne, a gabatar da duk wanda ake zargi gaban kotu, kuma a kwato kudaden al’umma.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...