SERAP ta kai karar Buhari kotu kan batan Naira biliyan 3

Date:

Daga Halima M Sadeeq

Kungiyar SERAP mai fafutukar yaki da cin hanci a Najeriya ta shigar da karar Shugaba Buhari gaban kotu “kan gaza gudanar da bincike game da zargin da ake yi na batan kudaden da suka kai naira biliyan 3 daga ma’aikatar kuɗi ta kasar, domin tabbatar da an gurfanar da wadanda ake zargi da hannu ciki da kuma kwato kudaden.”

Karar ta biyo bayan batan dabon da ake zargin da ofishin babban akanta janar na kasar ya shigar a 2018 da 2019 na rahoton da yake fitarwa, wanda aka batar da su ba bisa ka’ida ba ko kuma ba a bayar da bayanansu ba.

Sakon taya Murnar Samun shugabancin jam’iyyar SDP a Jihar Kano

BBC Hausa ta rawaito karar mai lamba FHC/L/CS/148/22 an shigar da ita ne a ranar Juma’ar da ta gabata a wata babbar kotun Tarayya da ke Lagos, kamar yadda SERAP ta bukata:

“umarnin da zai sanya Shugaba Buhari ya tabbatar da an gudanar da bincike game da zargin da ake yi na batan naira biliyan 3.1 wadanda kudaden mutanen Najeriya ne, a gabatar da duk wanda ake zargi gaban kotu, kuma a kwato kudaden al’umma.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Na sauke nauyin da Tinubu ya ɗora min – Gwamnan riko na jihar Rivers

Vice-Admiral Ibok-Ete Ibas (Mai ritaya), wanda shi ne gwamnan...

Cin Gashin Kan Kananan Hukumomi: Kawu Sumaila ya jinjinawa Gwamnan Kano

Sanatan da ke wakiltar Kano ta Kudu a Majalisar...

Gwamna Yusuf Ya Shirya Baiwa Kananan Hukumomin Kano Cikakken ‘Yan cin Kai

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...

Majalisar Zartarwa ta jihar Kano ta Amince da kashe Naira Biliyan 18 don aiwatar da wasu aiyuka

  Majalisar zartarwar jihar Kano karkashin jagorancin gwamna Abba Kabir...