Rikicin cikin gida yasa uwar jam’iyyar SDP bayan rushe shugabancinta a kano ta nada sabbi

Date:

Daga Sayyadi Abubakar

 

Uwar jam’iyyar SDP ta kasa ta amince da rushe shugabancin jam’iyyar na kano tare da kafa kwamitin rikon kwarya domin tafiyar da harkokin jam’iyyar a nan kano.

KADAURA24 ta rawaito Cikin wata wasika mai kwanan watan 14 ga watan wannan wata na janairu wasu jagororin jam’iyyar ta SDP a kano sun roki uwar jam’iyyar data rushe shugabancin jam’iyyar saboda wasu dalilai na rashen tafiyar da harkokin jam’iyyar yadda ya dace a jihar kano.

Wasikar koken mai dauke da sa hannun sakataren kwamitin tuntuba na jam’iyyar na kasa Yusuf Buhari da mambobin kwamitin na tuntuba Muhammad Bakin zuwa da Nastura ashir Sharif sun ce shugabancin baya gudanar da aikin kamar yadda aka dora masa kuma sun gaza ciyar da jam’iyyar gaba dai ma koma baya suke haifarwa jam’iyyar ta SDP a nan kano.

Tuni dai uwar jam’iyyar ta SDP ta kasa ta amince da rushe shugabannin jam’iyyar a kano tare da maye gurbinsu da kwamitin riko wanda ake sa rai zai tafiyar da harkokin jam’iyyar har na tsahon kwanaki 90.

Hon. Ali Shattima shi aka nada a Matsayin Shugaban Kwamitin rikon jam’iyyar a kano

Hon. Ali Shatima shugaba

Hon. Hussaini Mai Riga Sakatare

Alh. Sani Mahmud Vice central

Mallam Sale Matugwy Vice Chairman- South

Amb. Munir Sarki Adamu:
Sakataren tsare-tsare

Alh. Zangina Ahmed: Sakataren Yada Labarai

Alh. Abubakar Ibrahim Mukamin S Ma’aji

Barr. Nadia Ado sakatariyar harkokin shari’a

Alh. Abubakar Ali Ado Shugaban matasa

Hajiya Ummi Kabir shugabar mata

Rilwan Muhammed Gurduba: jami’in walwala

Alh. Yusuf Ali Shanono: mataimakin sakatare

Alh. Dahiru Abdullahi: mataimakin ma’aji

Alhaji. Yunusa Abdulkarim: mataimakin jami’in walwala

Cikin wata wasika mai dauke da sa hannun sakataren jam’iyyar SDP na kasa Alhaji Shehu Musa Gabam (Makaman Tilde) ya bukaci sabbin shugabannin jam’iyyar ta SDP a kano dasu hada kan yan jam’iyyar domin samun nasarar zabe mai zuwa na shekara ta 2023.

1 COMMENT

  1. An intriguing discussion is worth comment. I believe that you should publish more about this issue, it may not be a taboo subject but generally people don’t speak
    about these topics. To the next! Best wishes!!

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...