Twitter sun ce sun ji dadin dawo wa Nigeria

Date:

Dandalin sada zumunta na Twitter ya bayyana jin daɗinsa game da matakin gwamnatin Najeriya na dawo da ayyukan shafin a ƙasar bayan wata bakwai.

“Mun ji daɗi ganin cewa mutanen Najeriya na iya amfani da Twitter,” a cewar kamfanin.

“Muna matuƙar son yin aiki a Najeriya, inda ake amfani da Twitter don kasuwanci da sadar da al’adu da kuma tattaunawa,” in ji Twitter cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinnsa na dandalin ranar Alhamis.

A ranar Laraba ne wata sanarwa daga fadar gwamnati ta ce Shugaba Buhari ya amince a cire haramcin amfani da Twitter daga 12:00 na daren Laraba.

Gwamnati ta rufe shafin ne a watan Yunin 2021 bayan ya goge wani saƙo na Buhari kan ‘yan bindigar da ke tayar da hankali a yankin kudu maso gabashin ƙasar, tana mai zargin kamfanin da yaɗa labaran “raba kan ƙasa”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...