2023: Bayan Rikicin APC a Gombe, Jam’iyyar ta Sulhunta Danjuma Goje da Gwamna Yahaya Inuwa

Date:

Daga Abdulrasheed B Imam

 

Kwamitin Rikon Jam’iyar APC na Wucin-gadi, ƙarƙashin jagorancin Gwamnan Jihar Yobe Mai Mala Buni ya sulhunta tsakanin Gwamna Muhammad Yahaya Inuwa na Jihar Gombe da kuma abokin burmin sa na siyasa, tsohon gwamnan jihar, Sanata Ɗanjuma Goje.

Jami’in Yaɗa Labarai na Shugaban Kwamitin Rikon jam’iyyar, Mamman Mohammed ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Larabar data gabata a Abuja.

Sanarwar ta ce Buni, da Shugaban Kwamitin Sulhu na APC, Sanata Abdullahi Adamu da tsohon Gwamnan Jihar Borno Kashim Shattima, mamba a kwamitin, su ne su ka jagoranci sulhun.

Sanarwar ta ce wannan shi ne karon farko da manyan ƴan siyasar na Gombe su ka haɗu tun bayan da rigimar siyasa ta ɓarke tsakanin su a shekarar bara.

Mai Mala Buni, Matsayin sa na Shugaban Kwamitin Rikon jam’iyyar APC ta kasa ya baiyana jin daɗin sa game da sulhun da a ka yi.

Ya kuma yi alwashin sulhunta duk masu ruwa da tsaki a APC domin ƙarfafa jam’iyar yayin da a ke tunkarar kakar zaɓe ta 2023.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kano Ta Zama Zakara A Jarrabawa NECO Ta Bana

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Najeriya (NECO),ta fitar...

Kungiyar Karamci United Family ta Karrama Shugaban gidan Radiyon Pyramid Saboda Taimakawa Al’umma

Shugaban gidan Radio tarayya Pyramid FM Dr. Garba Ubale...

Kotu ta yanke hukunci kan ko ICPC tana da ikon gudanar da binciken kudin tallafin karatu na Kano

Babbar Kotun tarayya dake Babban Birnin Tarayya (FCT), karkashin...

Dalilan Hukumar tace fina-finai ta Kano na haramta muƙabalar tsakanin masu waƙoƙin yabon Ma’aiki S A W

Hukumar Tace Fina-finan Jihar Kano ta sanar da haramta...