Wani Yaro Dan Shekaru 4 Rasu Bayan ya fada Rijiya a Kano

Date:

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da mutuwar wani yaro mai shekaru hudu Mai Suna Mustapha Dalhatu a Kofar Dawanau dake karamar hukumar Ungoggo a jihar.
 Jami’in hulda da jama’a na hukumar SFS Saminu Yusif Abdullahi ya tabbatarwa manema labarai faruwar lamarin a kano.
 Ya bayyana cewa hukumar ta samu kiran ceto daga wani Aminu Sani Shu’aibu cewa wani karamin yaro ya fada cikin rijiya.
 Saminu Yusif ya yi nuni da cewa, da tawagar su ta isa ta yi nasarar ceto yaron Cikin Mawuyacin Halin, inda daga bisani jami’an lafiya suka tabbatar da mutuwarsa.
 Ya ce an mika gawar marigayin ga hakimin unguwar Dawanau, Alhaji Musa Habibu.
 Hakazalika, ‘yan kwana-kwana na jihar Kano sun kashe wata gobara da ta tashi a layin ‘Yan Robobi da ke Kasuwar Kofar Wambai a karamar hukumar Kano.
 Da yake bayyana lamarin kakakin hukumar ya ci gaba da cewa shago daya gobarar ta shafa.
 Ya ce babu wani rai da aka rasa a lokacin faruwar lamarin, sakamakon daukin gaggawar da hukumar kashe gobara ta Kano ta Kai Wajen.
 Jami’in hulda da jama’a ya bukaci jama’a da su tabbatar da daukar matakan hana Faruwar gobara a kowanni lokaci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...