Daga Abdulrasheed B Imam
Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar wakilai Hon Alhassan Ado Doguwa ya bayyana Rashin tsohon Tantakarar Shugabancin Kasar nan a zaben Shekara ta 1993 a Matsayin Babban rashi ga al’ummar Kasar nan baki daya.
Shugaban Masu Rinjayen Wanda shi ne Sardaunan Rano ya bayyana hakan ne Cikin Wata Sanarwa da Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Majalisar wakilai Auwal Ali Sufi ya aikowa Kadaura24.
Yace Sardaunan Rano ya kadu sosai Lokacin da ya Sami labarin Rasuwar Guda Cikin Dattawan Jihar Kano Alhaji Bashi Othman Tofa Wanda ya rasu Jiya litinin.
“Bashir Othman Tofa ya bada Gudunmawa sosai Wajen cigaba damokaradiyya da Ilimi a Jihar Kano da Kasa baki daya, don haka cike gibin da ya bari Zai yi wuya a nan kusa”. Hon Doguwa
Hon. Alhassan Ado Doguwa Dan Majalisar wakilai da yake wakiltar Kananan Hukumomin Doguwa da Tudun Wada yace a madadin Shi Kansa da iyalansa da al’ummar mazabar sa yana Mika Sakon ta’aziyyar sa ga Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero da iyalan mamacin da al’ummar Jihar Kano baki daya.
Sardaunan Rano ya yi fatan Allah ya gafarta tawa Bashir Othman Tofa ya baiwa iyalansa Hakurin jure Wannan gagarumin Rashi.