Daga Rukayya Abdullahi Maida
Hukumar Tace Fina Finai da daf’i ta Jihar Kano ta jadda kudirin ta nayin aiki kafada-kafada da ‘yan Jaridu domin yaki da cin zarafin Al,umma .
KADAURA24 ta rawaito Shugaban Hukumar Malam Isma’ila NaAbba Afakallah ne ya bayyana hakan a lokacin daya Karfi bakuncin Shuwagabannin Kungiyar Masu gabatar da shirin al’amuran Yau da kullum a radio Wato Magazine programme dake Jihar Kano a Ofishin sa.
Malam Afakallah yace ‘yan Jarida Suna da Mahimmanci wajen temakon Al’umma tare da magance kalubalen da Ake fuskan ta musamman a Gidajen kallo.
Afakallah ya kara da cewa yanzu lokaci yayi da Gidajen Radio zasu temaka wajen wayar da kan Iyaye mata akan Wani abu TIKTOK,,, Wanda yake bata tarbiyya.
Kazalika Shugaban Hukumar tace Fina-Finan ya godewa Kungiyar Masu gabatar da shirin Magazine programme din bisa basu hadin kai da goyan bayan da Suke yi wajen aiki tare.
Da yake nasa Jawabin Shugaban Kungiyar Commared Sani Abdurrazak Darma yace sun kai ziyarar ne domin kulla alaka Mai Karfi da Hukumar tare da Yin aiki tare da Juna,,
Commared Sani Darma yace Kungiyar tana aiki ne domin hada kan masu gabatar da shirin Magazine da kuma yin aiki tare a Juna.
A karshen Shugaban Kungiyar Masu gabatar da shirin na Magazine din ya bukaci Hukumar ta cigaba da bawa ‘yan Jaridu gudunmawa domin kawo cigaban Al,umma.
בעיות אין אונות בת ים דירות דיסקרטיות בירושלים