Ku Taimaka Wajen Wayar da Kan Iyaye illar TikTok – Afakallah ya Fadawa ‘Yan Jaridu

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Hukumar Tace Fina Finai da daf’i ta Jihar Kano ta jadda kudirin ta nayin aiki kafada-kafada da ‘yan Jaridu domin yaki da cin zarafin Al,umma .

KADAURA24 ta rawaito Shugaban Hukumar Malam Isma’ila NaAbba Afakallah ne ya bayyana hakan a lokacin daya Karfi bakuncin Shuwagabannin Kungiyar Masu gabatar da shirin al’amuran Yau da kullum a radio Wato Magazine programme dake Jihar Kano a Ofishin sa.

Malam Afakallah yace ‘yan Jarida Suna da Mahimmanci wajen temakon Al’umma tare da magance kalubalen da Ake fuskan ta musamman a Gidajen kallo.

Afakallah ya kara da cewa yanzu lokaci yayi da Gidajen Radio zasu temaka wajen wayar da kan Iyaye mata akan Wani abu TIKTOK,,, Wanda yake bata tarbiyya.

Kazalika Shugaban Hukumar tace Fina-Finan ya godewa Kungiyar Masu gabatar da shirin Magazine programme din bisa basu hadin kai da goyan bayan da Suke yi wajen aiki tare.

Da yake nasa Jawabin Shugaban Kungiyar Commared Sani Abdurrazak Darma yace sun kai ziyarar ne domin kulla alaka Mai Karfi da Hukumar tare da Yin aiki tare da Juna,,

Commared Sani Darma yace Kungiyar tana aiki ne domin hada kan masu gabatar da shirin Magazine da kuma yin aiki tare a Juna.

A karshen Shugaban Kungiyar Masu gabatar da shirin na Magazine din ya bukaci Hukumar ta cigaba da bawa ‘yan Jaridu gudunmawa domin kawo cigaban Al,umma.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...