Covid-19: An Daina Hada Sahun Sallah a Masallacin Ka’aba da na Annabi dake Madina

Date:

An dawo da dokar tilasta bayar da tazara da saka takunkumi a Masallacin Ka’aba a Makkah da kuma na Annabi a Madina, kamar yadda hukumomin da ke kula da Masallatan Biyu Masu Daraja na Saudiyya suka bayyana.

Matakin zai fara aiki ne daga ranar Alhamis, inda hukumomin suka ce yanzu saka takunkumi da bayar da tazara ya zama wajibi.

Hukumomin sun ce matakin ya shafi masu aikin Umrah da masu ɗawafi da sauran masu Ibada a masallatan biyu.

Sannan an yi gargaɗi ga baƙi da ma’aikatan Masallatan biyu su mutunta dokar.

Dokokin za su rika aiki a cikin gidaje da kuma waje inda mutane ke mu’amalar yau da kullum.

A ‘yan kwanakin nan masu kamuwa da korona na karuwa a Saudiyya

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kamata ya yi wajen Mauludi ya Zama waje Mai nutsuwa saboda ana ambaton Allah da Manzonsa – Mal Ibrahim Khalil

Shugaban Majalisar shuhurar Malamai ta jihar Kano Sheikh Malam...

Ra’ayi:‎Tsarin Kwankwasiyya ya dora Kano a gwadaben cigaba a mulkin Gwamna Abba Kabir -Adamu Shehu Bello

‎ ‎Ra’ayi ‎ ‎Daga Adamu Shehu Bello (Bayero Chedi), Jigo a Kwankwasiyya...

Al’ummar Garin Riruwai da wani Kamfanin Hakar ma’adanai Sun Cimma Yarjejeniya Kan Ci gaban yankin

Kwamitin ci gaban Al’ummar garajn Riruwai da wani kamfanin...