Ƴan Sanda sun cafke ƙasurgumin ɗan fashin daji, Mai-ƴanmata a Zamfara

Date:

 

Rundunar Ƴan Sanda ta Jihar Zamfara ta tabbatar da cafke wani ƙasurgumin ɗan fashin daji, Sani Mati, wanda a ka fi sani da Mai-ƴanmata a jihar.

Rundunar ta ce Mai-ƴanmata, ɗan shekara 20 kacal da haihuwa, ya ƙware wajen garkuwa da mutane, fashin daji, satar shanu da sauran manyan laifuka a yankin Shinkafi, Zurmi da Birnin Magaji a Zamfara.

Kwamishinan Ƴan Sanda na Jihar Zamfara, Ayuba N. Elkanah ne ya baiyana haka a taron manema labarai yayin da rundunar ta yi holon ɗan ta’addan a juya Laraba.

A cewar Kwamishinan, ” a ranar 28 ga Disamba da misalin ƙarfe 5 na yamma, yayin da su ke wani sintiri na sirri bayan sun samu bayanan sirri, sun cafke wani ƙasurgumin ɗan fashin daji mai suna Sani Mati, wanda a ka fi sani da Mai-ƴanmata ɗan ƙauyen Mayasa a Ƙaramar Hukumar Zurmi.

Ya ƙara da cewa Mai-ƴanmata ya shiga komar ƴan sanadan ne lokacin yana shirin sanya shinge ya tsare bayin Allah domin ya yi garkuwa da su a daidai wani ƙauye mai suna Koliya.

Daily Nigerian ta rawaito Elkanah ya ƙara da cewa da a ɓangaren Turji Mai-ƴanmata ya ke, inda yanzu ya koma sansanin wani ƙasurgumin ɗan fashin daji mai suna Kachalla Sani Black.

Ya ce an samu bindiga samfurin AK-47, sai kwanson harsashi 2, sai harsashi 3 da kuma babur guda 1.

Ya ce a na nan a na yi masa tambayoyi inda da ga nan za a ki shi kotu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...