Yanzu-Yanzu: Ganduje ya je yiwa Kwankwaso ta’aziyyar kaninsa

Date:

Daga Zara Jamil Isa

Gwamanan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya jagoranci tawagar Gwamnatin Jihar Kano zuwa Garin Kwankwaso dake Karamar Hukumar Madobi don yin ta’aziyyar Kanin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso Kwamaret Inuwa Musa Kwankwaso.
Kadaura24 ta rawaito Idan ba’a mantaba inuwa Kwankwaso Wanda yake shakikin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya rasu ne a Jiya talata ,Inda akai Masa sutura a jiyan kamar yadda addinin Musulci yayi tanadi.
Yayin ta’aziyyar Gwamna Ganduje ya yiwa mamacin addu’a da fatan samun rahamar Ubangiji tare da Allah zai baiwa iyalai da yan uwan Marigayin Hakurin jure rashin.
Hakimin Madobi Makaman Karewa Alhaji Musa Sale Musa ne ya tarbi tawagar Gwamnan tare da godewa Gwamnan bisa ziyarar ta’aziyyar Dan uwansu da yaje musu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...

RMK@69: Kwankwaso Jagora Ne Mai Hangen Nesa, Abba Kuma Na Kawo Ci Gaba a Kano – Bakwana

Wani jigo a kungiyar Kwankwasiyya, kuma tsohon mai ba...

Da dumi-dumi: Tinubu ya nada sabon Minista

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya aike da sunan...

Kashim Shattima ya sauka daga kujerar ta mataimakin shugaban Nigeria ya baiwa wata yarinya

Mataimakin shugaban Kasa Kashim Shattima ya sauka daga kujerarsa...