Kotu ta bada Umarnin Dakatar da Rushe Kasuwar Garin Bichi

Date:

Daga Rabi’u Sani Hassan
Babba Kotu Jahar Kano Mai Lambar 16 dake Miller road Karkashin Jagoranci Mai Sharia Jamilu Shehu Sulaiman ta bada Umarnin dakatar da Karamar hukumar Bichi daga rushe Kasuwar Bichi da tashin su zuwa lokaci da kotu zata saurare karar da wasu ‘yan kasuwa suka shigar gabatan ta.
KADAURA24 ta rawaito takardar karar mai dauke da sunayen Alh Haladu Bichi, Alh Umar Isa, Alh Zilyadani Bichi, Alh Sunusi Bako, Abdullahi Iliyasu, Abubakar Murtala da kuma Murtala Umar a Matsayin Wadanda su ka yi karar Karamar hukumar Bichi ta tare da Shugaban Karamar hukumar ta Bichi ta hannu Lauyansu Barrister A. I. Ma’aji a madadin Sauran yan Kasuwar ta Bichi.
Ta cikin takardar karar sun zargi Karamar hukumar Bichi da tashin su daga Kasuwar ba tare da wani gamsasshen bayani ba.
Sai dai a zaman kotun bisa jagorancin mai shari’a Jamilu Shehu Sulaiman kotun ta ba karamar hukumar umarnin dakatawa daga rushe Kasuwar ko tashin ‘yan kasuwar har sai ta saurarin Kara zuwa 2/2/2022.
Idan ba’a manta a satin da ya gabata ne aka fara rushe Kasuwar ta Bichi da nufin sauya Mata fasali zuwa na Zamani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...