Kotu ta bada Umarnin Dakatar da Rushe Kasuwar Garin Bichi

Date:

Daga Rabi’u Sani Hassan
Babba Kotu Jahar Kano Mai Lambar 16 dake Miller road Karkashin Jagoranci Mai Sharia Jamilu Shehu Sulaiman ta bada Umarnin dakatar da Karamar hukumar Bichi daga rushe Kasuwar Bichi da tashin su zuwa lokaci da kotu zata saurare karar da wasu ‘yan kasuwa suka shigar gabatan ta.
KADAURA24 ta rawaito takardar karar mai dauke da sunayen Alh Haladu Bichi, Alh Umar Isa, Alh Zilyadani Bichi, Alh Sunusi Bako, Abdullahi Iliyasu, Abubakar Murtala da kuma Murtala Umar a Matsayin Wadanda su ka yi karar Karamar hukumar Bichi ta tare da Shugaban Karamar hukumar ta Bichi ta hannu Lauyansu Barrister A. I. Ma’aji a madadin Sauran yan Kasuwar ta Bichi.
Ta cikin takardar karar sun zargi Karamar hukumar Bichi da tashin su daga Kasuwar ba tare da wani gamsasshen bayani ba.
Sai dai a zaman kotun bisa jagorancin mai shari’a Jamilu Shehu Sulaiman kotun ta ba karamar hukumar umarnin dakatawa daga rushe Kasuwar ko tashin ‘yan kasuwar har sai ta saurarin Kara zuwa 2/2/2022.
Idan ba’a manta a satin da ya gabata ne aka fara rushe Kasuwar ta Bichi da nufin sauya Mata fasali zuwa na Zamani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Nasarar da Ɗaliban Kano suka Samu a NECO Kokari ne na Gwamnatin Ganduje – Sanusi Kiru

Tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Hon. Muhammad Sanusi...

Gwamnatin Tarayya ta Kaddamar da Aikin samar da wutar sola na Naira Biliyan 12 a asibitin Malam Aminu Kano

Kwana biyu bayan rikicin wutar lantarki tsakanin Asibitin Koyarwa...

Kano Ta Zama Zakara A Jarrabawa NECO Ta Bana

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Najeriya (NECO),ta fitar...

Kungiyar Karamci United Family ta Karrama Shugaban gidan Radiyon Pyramid Saboda Taimakawa Al’umma

Shugaban gidan Radio tarayya Pyramid FM Dr. Garba Ubale...