Allah ya yiwa Sarkin Ban Kano Rasuwa

Date:

Daga Tijjani Mu’azu Aujara

 

Allah ya yiwa tsohon Hakimin karamar hukumar Dambatta, kuma kwamishinan ilimi na farko a jihar Kano Alhaji Mukhtar Adnan rasuwa.

 

Daya daga cikin ‘ya’yansa Baba Ado ne ya tabbatar wa da BBC labarin rasuwar tasa.

Ya ce ya rasu ne dab da asubahin ranar Juma’a a sibitin UMC Zahir da ke unguwar Jan Bulo inda ya yi jinya

Marigayi Alhaji Mukhtar Adnan ya zama dan majalisar sarki mai nadin sarki tun a shekarar 1954, inda bayan shekaru 9 da samun wannan mukamin a fadar Sarkin Kano ne, suka nada marigayi Dr. Ado Bayero a matsayin Sarkin Kano a shekara ta 1963.

Daily News24 ta rawaito Marigayi Sarkin Ban Kano Alhaji Mukhtar Adnan shi ne kwamishinan Ilmi na farko tun a tsohuwar jihar Kano, haka zalika ya taba rike bulaliyar majalisar tarayyar Najeriya.

A lokacin Gwamnatin Malam Ibrahim Shekarau ne aka sanya sunan marigayin a Kwalejin Kimiyya ta maza dake kan titin State Road wato ‘Day Science‘.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...