Tsaftar Muhalli: An Kama Mutane 111 da karya Dokar tsaftar Muhalli a Kano

Date:

  1. Daga Sani Abdulrazak Darma
Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewar a shirye take ta cigaba da bayar da kulawa ga Al’umma domin kula da Muhallan su.
Kwamishinan Muhalli  Dr Kabiru Ibrahim Getso ne ya bayyana hakan, yayin zagayen Tsaftar Mahalli na karshen wata-wata.
Dr Kabiru Getso yace Gwamnatin Dr Abdullahi Umar Ganduje ,ta himmatu wajen tsaftace Muhalli domin kawar da Duk wata cuta da take yaduwa a cikin Al’umma.
Kwamishinan Muhallin yace an Samar da wannan tsari na gyara Muhalli na karshen wata ne, domin Al’umma su zauna a Gidajen su, don kawar da duk wata kazanta da take tattara a Mahallan al’umma.
Wakilin Kadaura24 Sani Abdurrazak Darma ya rawaito mana cewa yayin gudanar da zagayen Tsaftar Mahallin, an samu mutane 111 wadanda suka karya doka Kuma aka ci tarar su kudi naira 123,200 Wanda kotun tafi da gidan ka suka kama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...