Tsaftar Muhalli: An Kama Mutane 111 da karya Dokar tsaftar Muhalli a Kano

Date:

  1. Daga Sani Abdulrazak Darma
Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewar a shirye take ta cigaba da bayar da kulawa ga Al’umma domin kula da Muhallan su.
Kwamishinan Muhalli  Dr Kabiru Ibrahim Getso ne ya bayyana hakan, yayin zagayen Tsaftar Mahalli na karshen wata-wata.
Dr Kabiru Getso yace Gwamnatin Dr Abdullahi Umar Ganduje ,ta himmatu wajen tsaftace Muhalli domin kawar da Duk wata cuta da take yaduwa a cikin Al’umma.
Kwamishinan Muhallin yace an Samar da wannan tsari na gyara Muhalli na karshen wata ne, domin Al’umma su zauna a Gidajen su, don kawar da duk wata kazanta da take tattara a Mahallan al’umma.
Wakilin Kadaura24 Sani Abdurrazak Darma ya rawaito mana cewa yayin gudanar da zagayen Tsaftar Mahallin, an samu mutane 111 wadanda suka karya doka Kuma aka ci tarar su kudi naira 123,200 Wanda kotun tafi da gidan ka suka kama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...