RUWASA ta fi kowacce hukuma kazanta cikin shekaru 2 a Kano – Dr Kabiru Getso

Date:

By Sani Magaji Garko

Maaikatar Muhalli ta jihar Kano ta ce bata taba ganin hukuma Mai kazanta cikin shekaru biyu ba kamar hukumar samar da ruwansha a jihar Kano.

Kadaura24 ta rawaito Kwamishinan Muhalli na jihar Kano Dakta Kabiru Ibrahim Getso ne ya bayyana hakan lokacin tsaftar Muhallin ta Kasuwanni da maaikatu da hukumomin Gwamnatin wacce ake gudanarwa a duk juma’ar karshen wata a nan Kano.

Kwamishinan ya ce maaikatar Muhallin ta Kuma bawa Hukumar waadin kwanaki 3 da su tsaftace muhallansu ko kuma maaikatar ta dauki mataki na gaba.

Dakta Kabiru Getso ya kuma yabawa hukumar kula da gandun daji ta jihar Kano karkashin Sa’idu Gwadabe Gwarzo dangane da yadda suke kula da tsaftar Muhalli inda ya kara da cewa ya umarci daraktan da ke kula da gurbacewar Muhalli da su ziyarci gidan gandun dajin domin bada shawarar yadda zaa yashe Magudanan ruwanta da suka toshe.

Kwamishinan ya kuma ce maaikatar zata duba yadda zaa kammala ginin sabbin bandakunan da ake aikin su yanzu haka a gidan

A jawabinsu daban-daban, shugaban Hukumar Kula da gandun daji na jihar Kano Sa’idu Gwadabe Gwarzo Wanda Amina Muhammad Dankadai ta wakilta da shugaban Hukumar kula da tashoshin motar Kano Line Nasiru Aliko Koki Wanda Rabilu Hamisu Garin-Danga ya wakilta sun bayyana farin cikin su dangane da ziyarar inda suka bada tabbacin dorewar kula da tsaftar Muhallin.

Daga bisani kwamishinan Muhalli ya ja kunnen matuka baburan Adaidaita sahu da Samari da suke fitowa kwallon kafa da su guji karya dokar tsaftar Muhalli inda ya duk Wanda aka kama zaa hukunta shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...