Allah ya yiwa Sarkin Tsaftar Kano Rasuwa a Kasar Saudia

Date:

Daga Ibrahim Sani Mai Nasara
An sanar da rasuwar Sarkin Tsaftar Kano Alhaji Jafar Ahmed Gwarzo a yau Laraba.
 Alhaji Jafar ya rasu ne a yau bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya a kasar Saudiyya.
 Kafin rasuwarsa, Sarkin ya kasance babban mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Kano Abdullahi Ganduje kan rigakafin cutar shan inna.
 Da yake tabbatar da rasuwar sa ga manema labarai, wani makusanci marigayin Alhaji Nasiru Sani Gwarzo ya ce, marigayi Jafar Gwarzo ya tafi kasar Saudiyya domin yin Umrah kwanakin baya.
 Marigayin ya rasu ya bar mata da ’ya’ya da dama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Nazarin Yadda Shaharar Sanata Barau Ta Karade Nigeria – Abba Anwar

Daga Abba Anwar Wani babban abin lura game da rayuwar...

Kungiyar Ɗaliban Mariri ta gudanar da aikin duba marasa Lafiya kyauta a yankin

Daga Abdallahi Shu'aibu Hayewa   Kungiyar Dalibai ta Makarantar Mariri wato...

Gwamnan Taraba ya bayyana dalilinsa na shirin komawa APC

Gwamnan jihar Taraba, Agbu Kefas, ya ce zai shiga...

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...