Allah ya yiwa Sarkin Tsaftar Kano Rasuwa a Kasar Saudia

Date:

Daga Ibrahim Sani Mai Nasara
An sanar da rasuwar Sarkin Tsaftar Kano Alhaji Jafar Ahmed Gwarzo a yau Laraba.
 Alhaji Jafar ya rasu ne a yau bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya a kasar Saudiyya.
 Kafin rasuwarsa, Sarkin ya kasance babban mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Kano Abdullahi Ganduje kan rigakafin cutar shan inna.
 Da yake tabbatar da rasuwar sa ga manema labarai, wani makusanci marigayin Alhaji Nasiru Sani Gwarzo ya ce, marigayi Jafar Gwarzo ya tafi kasar Saudiyya domin yin Umrah kwanakin baya.
 Marigayin ya rasu ya bar mata da ’ya’ya da dama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

‎Kawu Sumaila ya binciko kudaden da gwamnatin tarayya ta turawa kananan hukumomin Kano

‎ ‎Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Suleiman Abdulrahman Kawu...

Kamata ya yi wajen Mauludi ya Zama waje Mai nutsuwa saboda ana ambaton Allah da Manzonsa – Mal Ibrahim Khalil

Shugaban Majalisar shuhurar Malamai ta jihar Kano Sheikh Malam...

Ra’ayi:‎Tsarin Kwankwasiyya ya dora Kano a gwadaben cigaba a mulkin Gwamna Abba Kabir -Adamu Shehu Bello

‎ ‎Ra’ayi ‎ ‎Daga Adamu Shehu Bello (Bayero Chedi), Jigo a Kwankwasiyya...