Shugaba Buhari zai tsaida ranar babban taron jam’iyyar APC

Date:

Daga Jidda Abubakar
 Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai yanke hukunci Dangane da Ranar da jam’iyya mai mulki ta APC ta Kasa zata gudanar da Babban taron jam’iyyar ta kasa.
 Shugaban kungiyar gwamnonin jam’iyyar APC, Gwamna Atiku Bagudu na jihar Kebbi ya shaida wa manema labarai hakanda bayan kammala taron gwamnonin, Inda yace za su nemi ganawa da shugaban kasa domin Sanya ranar da ta dace.
 Ana kyautata zaton cewa Gwamnonin za su kuma nemi goyon bayan Shugaban kasa kan yadda ake ta cece-kuce a kan batun Zaben fidda gwani na kato bayan Kato a cikin jam’iyyun siyasar Kasar nan tsakanin ‘yan majalisar dokokin Najeriya da jam’iyyun siyasa ciki har da babbar jam’iyyar adawa ta PDP.
 Haka kuma Gwamnonin sun bayyana ji dadinsu Kan yadda zaben Gwamnan Anambra ya gudana cikin kwanciyar hankali.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...