Gobara ta yi barna a Jami’ar KUST ta Wudil Dake Kano

Date:

Daga Nura Abubakar
Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ce ta kashe gobarar da ta kone ofisoshi guda biyar, a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Kano dake Wudil (KUST) a Kano.
 Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Alhaji Saminu Abdullahi ya raba wa manema labarai ranar Lahadi a Kano.
 “Mun samu kira a sashin mu na Wudil daga jami’an tsaro da misalin karfe 12:04 na safe cewa gobara ta tashi a wani benen Jami’ar.
 Bayan samun labarin, mun aika da motar kashe gobara zuwa wurin da abin ya faru da misalin karfe 12:07 na safe, domin shawo kan lamarin,” in ji sanarwar.
 Abdullahi ya bayyana cewa gobarar ta kone dukkan ofisoshin guda biyar gaba daya.
 Ya kara da cewa wutar lantarki ce ta haddasa gobarar.
 Ya bukaci jama’a da su kara yin taka-tsan-tsan da kuma daukar matakan kariya domin gudun tashin gobara Musamman a Wannan Lokaci da sanyi yake kara kamari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...