Yanzu-Yanzu: Ganduje ya yiwa Majalisar Zartarwa ta jihar kano Garanbawul

Date:

Daga khadija Abdullahi

Gwaman jihar kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje bayan ya rantsar da sabon kwamishina Engr. Idris wada Sale wanda majalisar dokokin jihar kano ta amince da nada shi a matsayin kwamiahina, ya gudanar da sauye-sauye a cikin majalisar zartarwar jihar kano.
Kadaura24 ta rawaito Ganduje ya jagoranci rantsar da sabon kwamishinan ne a yayin taron majalisar zartarwar jihar kano na wannan makon wanda ake gudanarwa a gidan gwamnatin kano.
Gwamnan yace sabon kwamishinan an tura shi ma’aikatar aiyuka ta jiha ,yayin da kwamishinan dake Ma’aikatar wato Idris Garba Unguwar Rimi aka mayar da shi ma’aikatar kimiyya fasaha da ƙirƙira ta jihar kano.
Sabon kwamishinan dai kafin wannan lokaci shi ne manajan daraktan hukumar karma ta jihar kano .
Tuni dai kwamishinan ya fara aiki domin ya zauna zaman majalisar zartarwar jiha na wannan makon.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...