Za’a yi zafin Rana da tsayawa Mai yawa daga Juma’a zuwa lahadi a Nigeria – Nimet

Date:

Hukumar Hasashen Yanayi ta Najeriya Nimet, ta yi hasashen cewa za a yi zafin rana da kuma tsawa daga ranar Juma’a har zuwa Lahadi.

A bayanin hasashen da ta fitar a ranar Alhamis a Abuja babban birnin ƙasar, Nimet ta ce za a ƙwalla rana a yankin arewaci a ranar Juma’a da kuma yiwuwar yin tsawa a wasu yankunan Taraba da safiyar Juma’ar.

Sannan hukumar ta ce ana sa ran za a yi ta jera tsawa a Adamawa da Taraba da kuma kudancin Borno a yinin ranar.

“Hadari zai yi ta haɗuwa amma rana za ta dinga fitowa jifa-jifa a yankin arewa ta tsakiya tare da yin tsawa a wasu yankunan jihohin Filato da Nasarawa da Neja da Binuwai da kuma Abuja da rana da yamma,” a cewar hukumar.

Ta kara da “Hadari zai yi ta haɗuwa a biranen da ke kusa da gaɓar teku ama ba za ayi tsawa ba a jihohin Ogun da Akwa Ibom da safiyar.”

“Can da rana kuma ana sa ran za a yi ta tsawa a wasu yankunan jihohin Imo da Abia da Ebonyi da Osun da Lagos da Rivers da Bayelsa da Delta da Cross River da kuma Akwa Ibom,” a cewar Nimet.

Sanarwar Nimet ta kuma ce ana hasashen za a ƙwalla rana a arewaci tare da yiwuwar yin tsawa da safe a yankunan jihohin Adamawa da Taraba da Borno da Yobe da kuma Jigawa ranar Asabar.

Sannan za a yi tsawa a biranen Kano da Kaduna da Katsina da Zamfara da SOkoto da Kebbi da Bauchi da rana da yamma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...