Zaben APC: Musa Iliyasu kwankwaso yayi Zazzafan Martani ga Mal Ibrahim Shekarau

Date:

Daga Nura Abubakar Bichi

Kwamishinan Raya karkara da cigaban al’umma na Jihar Kano Hon. Musa Iliyasu kwankwaso ya bayyana cewa duk yadda Gwamna Abdullahi Ganduje ya dama Haka za’a Sha a Kano.

Musa Iliyasu kwankwaso ya bayyana hakan a taron Masu Ruwa da tsaki da Gwamna Ganduje ya kirawo a nan domin tattaunawa Kan al’amuran da suka Shafi jam’iyyar APC.

Musa Iliyasu yace Yanzu Abdullahi Umar Ganduje ne Gwamnan Kano Kuma ya Zama wajibi kowa ya bi duk wani abun daya fito dashi in dai a Kano ne.

” A Wannan dakin taro Kabiru Gaya yayi abun da yake so Kwankwaso yayi ,shima Malam Ibrahim Shekaraun yayi yadda yake so, to shima Ganduje tunda shi ne Gwamnan Kano dole abi abun da yace.” Inji Musa Kwankwaso

Kadaura24 ta rawaito Cewa a baya dai Musa Iliyasu kwankwaso ya yiwa Malam Ibrahim Shekarau Kwamishina Lokacin Yana Gwamnan Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...