Akwai yiwuwar Buhari Zai sake Korar Ministoci

Date:

Akwai yiwuwar Shugaba Muhammadu Buhari ya sake korar wasu ministocin Najeriya bayan kammala taron bin diddigin ayyukansu da za a kammala yau a Abuja.

Taron na kwana biyu karkashin jagorancin shugaban kasar an soma shi ne a jiya Litinin domin bitar ayyukan ministocin da nasarorin da suka samu ko akasin haka.

Taron ya samu halartar dukkanin ministoci da manyan sakatarorin ma’aikatun gwamnati da manyan jami’a.

Buhari ya ce zai zauna har zuwa karshen taron domin sauraron bayanan kowanne minista da kuma nasarori da yanayin ayyukansu cikin shekaru biyu da suka gabata.

A lokacin gabatar da jawabinsa, Shugaba Buhari ya gargadi ministocin da manyan sakatarorin ma’aikatu su mayar da hankali wajen ayyukan da ya rayata a wuyansu domin ci gaban gwmanatinsa.

A watan Satumba shugaban ya kori ministocinsa biyu na noma da wutar lantarki kan rashin taka rawar gani a ayyukansu.

Kuma sun kasance ministocin farko da Buhari ya kora tun hawansa mulki a 2015.

2 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...