Sojoji sun hallaka yan Bindiga da dama a Katsina da Sokoto

Date:

Sojojin Najeriya sun yi nasarar hallaka ɓarayin daji da dama tare da lalata maɓoyarsu a dazukan jihohin Sokoto da Katsina a yankin arewa maso yamma, kamar yadda jaridar intanet ta PRNigeria ta ruwaito.

A jihar Sokoto sojojin ƙarƙashin shirin HADARIN DAJI sun kai hare-hare ne ta sama a dazukan Mashema da Yanfako da Gebe da Gatawa a ƙananan hukumomin Isaa da Sabon Birni.

Wata kafa ta sojojin Najeriyar ta sheda wa jaridar ta PR cewa an samu nasarar hakan ne a ruwan bama-bamai da suka yi ranar biyar ga watan Oktoba 2021, bayan binciken da aka yi ta yi ta sama inda aka gano wuraren da ɓarayin dajin ke zaune.

Rahotan ya bayyana cewa mutanen yankunan da aka kai hare-haren sun bayar da labarin cewa sun ga ɓarayin da ke tserewa sun fake a wata makarantar furamare a ƙauyen Bafarawa.

A jihar Katsina jaridar ta PRNigeria ta ce ta gano cewa jiragen yaƙin sama na Najeriya sun yi ruwan bama-bamai a maɓoyar ɓarayin a dajin Rugu da ke da iyaka da Karamar Hukumar Ƙanƙara a tsakanin ranar 30 ga watan Satumba da 3 ga watn Oktoba na wanan shekara.

A ɗaya daga cikin hare-haren an lalata sansanin wani ɗan ta’adda da ake kira Gajere inda aka kashe yaransa 34, wasu kusan 20 kuma suka samu raunuka in ji rahoton jaridar.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...