Abduljabar: Matakin da Ganduje ya Dauka Kan Abduljabar abun yabo ne – Kungiyar JNI

Date:

Kungiyar Agaji Tara kasa reshen jahar Kano ta yabawa Gwamnatin jahar Kano bisa girmama addinin musulunci da malamai da takeye.

Shugaban kungiyar na jahar Kano Muhd Nuruddeen Lawan Gwagwarwa ne ya baiyana haka a sakonsa na barka da sallah ga al’ummar musulmi.

Yace gwamnatin jihar Kano tayi abun a yaba Mata Saboda da Matakin data dauka akan Wani Malami da yasu Kawo rudani da raba Kan mabiya addinin Musulunci.

Yace Yana Taya daukacin al’ummar musulmi Kano Dana Nigeria Baki daya Murnar zagayowar idin Babbar Sallah, Inda ya bukaci al’umma su cigaba da yin koyi da aiyukan alkhairin da Suka gabatar a kwanaki 10 Farko na Watan zulhijja.

Alhaji Nuruddeen Gwagwarwa ya Kuma yabawa malamai bisa addu’o’i da ilimantarwa da wayar dakan al’umma da suke akoyaushe, Sannan yayi kira ga al’ummar musulmi dasu kasance masu bin tsarin shari’ar musulunci a dukkan lamuransu na yau da kullun.

Shugaban Kungiyar ya Kuma yi kira ga Malamai a jihar nan dasu karfafa tsarin hadinkai, fahimtar juna da zaman lafiya a tsakanin alumma’a. A kashe ya Kuma yi kira ga al’umma dasu cigaba da adu’o’in samun zaman lafiya Mai dorewa a Kano da Kasa baki daya

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Daura ya nuna inda za’a binne shi idan ya rasu.

  Mai Martaba Sarkin Daura dake jihar katsina Alhaji Dr....

Na sauke nauyin da Tinubu ya ɗora min – Gwamnan riko na jihar Rivers

Vice-Admiral Ibok-Ete Ibas (Mai ritaya), wanda shi ne gwamnan...

Cin Gashin Kan Kananan Hukumomi: Kawu Sumaila ya jinjinawa Gwamnan Kano

Sanatan da ke wakiltar Kano ta Kudu a Majalisar...

Gwamna Yusuf Ya Shirya Baiwa Kananan Hukumomin Kano Cikakken ‘Yan cin Kai

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...