An tsinci Gawar Wani Jariri a Gezawa

Date:

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da mutuwar wani jariri dan kwana daya da aka samu a cikin wata rijiya a Garin Tsalle da ke Karamar Hukumar Gezawa.


 Jami’in hulda da jama’a na hukumar Saminu Yusuf Abdullahi ya bayyana cewa, ana zargin cewa wasu da ba a san ko su wanene ba sun jefar da sabon jaririn a cikin rijiyar .


 Ya lura cewa hukumar kashe gobara ta jihar kano ta samu kiran gaggawa daga wani jami’in ta Abubakar Ibrahim Dandago, yana mai cewa Jami’an Rundunar na agaji ba su bata lokaci wajen dauke gawar jaririn da ya mutu daga rijiyar.


 Haka kuma, wani mutum mai suna Babawo Sulaiman dan shekara 35 ya rasa ransa a yayin wata gobara a wani wurin walda da ke titin Airport Road a Sabon Gari Kano.


 A cewar jami’in hulda da jama’a, mutum uku ne lamarin ya shafa wanda ya rasa ransa yayin da wasu ke karbar magani a asibitin kwararru na Murtala Muhammad.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...