An tsinci Gawar Wani Jariri a Gezawa

Date:

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da mutuwar wani jariri dan kwana daya da aka samu a cikin wata rijiya a Garin Tsalle da ke Karamar Hukumar Gezawa.


 Jami’in hulda da jama’a na hukumar Saminu Yusuf Abdullahi ya bayyana cewa, ana zargin cewa wasu da ba a san ko su wanene ba sun jefar da sabon jaririn a cikin rijiyar .


 Ya lura cewa hukumar kashe gobara ta jihar kano ta samu kiran gaggawa daga wani jami’in ta Abubakar Ibrahim Dandago, yana mai cewa Jami’an Rundunar na agaji ba su bata lokaci wajen dauke gawar jaririn da ya mutu daga rijiyar.


 Haka kuma, wani mutum mai suna Babawo Sulaiman dan shekara 35 ya rasa ransa a yayin wata gobara a wani wurin walda da ke titin Airport Road a Sabon Gari Kano.


 A cewar jami’in hulda da jama’a, mutum uku ne lamarin ya shafa wanda ya rasa ransa yayin da wasu ke karbar magani a asibitin kwararru na Murtala Muhammad.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...