Hukumar Alhazai ta Kano zata fara Mayarwa Maniyata Kudinsu- Muhd Danbatta

Date:

Daga Halima M Abubakar

Hukumar Jin Dadin alhazai ta jihar Kano tace zata fara mayarwa Maniyata Aikin Hajjin bana kudaden su, Sakamakon Hana zuwa Aikin Hajjin da Kasar Saudiyya tayi Saboda Corona.

Sakataren Zartarwar Hukumar Alhaji Muhd Abba Danbatta ne ya bayyana hakan Yayin ganawarsa da Kadaura24 a ofishinsa.

Alhaji Muhd Abba Danbatta yace a Yau din Nan alhamis Hukumar zata Kara Kwamitin da Zai mayarwa Maniyatan kudaden da Suka Fara baiwa Hukumar.

Yace Kwamitin Zai Hadar da Masu Ruwa da tsaki a Hukumar da Kuma jami’ai daga Hukumomin Tsaro da Jami’i Daga Hukumar Hana cin hanci da rashawa domin Samun nasarar mayarwa Maniyata Kudinsu.

Yace kowanne lokaci Daga yanzu Maniyata zasu iya zuwa su karbi Kudinsu , sai dai yace za’a bada kudin ne ta banki da a Hannu ba.

Idan za’a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito a Ranar 11 ga watannan Hukumomi a Kasar Saudiyya Suka bayyana cewa baza su karbi Bakin Maniyata Aikin Hajjin bana ba Saboda Corona.

Shekaru biyu Kenan Corona tana Hana Aikin Hajjin a Dan Wannan taki.

322 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...