El-Rufa’i ya Kori Mutane 19 Daga Gwamnatinsa

Date:

Daga Safyan Dantala Jobawa

Gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya amince da korar masu taimaka masa na musamman guda 19 daga aiki.

A cewar wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar a yau Laraba, wannan ne zagayen farko na masu muƙamana siyasa da za a kora a yunƙurin da gwamnan ke yi na rage yawan ma’aikatan gwamnati.

Daga cikin waɗanda aka kora akwai mataimakin shugaban ma’aikatan gidan gwamnati da babban darakta a hukumar Public Procurement Authority.

Gwamna El-Rufai ya sha suka game da korar ma’aikata kusan 7,000 da ya yi, abin da ya jawo yajin aikin ma’aikata na kwana huɗu a jihar.

Sai dai gwamnatin na kare matakin da cewa tana kashe kusan kashi 80 cikin 100 na kuɗin da take samu wajen biyan albashi.

95 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Nan gaba kadan za mu bayyana sunayen masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Najeriya – Babban Hafsan tsaro

Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya ce...

Wasu yan daba sun ajiye Makamansu a Kano

Gwamnatin Jihar Kano Hadin gwaiwa da Rundunar Yansandan Jihar...

Masu Mukamai a gwamnatin Kano ba su da uzurin kin taimakawa yan Kwankwasiyya – Sanusi Bature

Mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin...

Magoya bayan Barr Ibrahim Isa (Matawallen Gwagwarwa) sun aikawa Gwamnan Kano Budaddiyar Wasika

Daga Isa Ahmad Getso Kira don nemawa Barr. Ibrahim Isa...