El-Rufa’i ya Kori Mutane 19 Daga Gwamnatinsa

Date:

Daga Safyan Dantala Jobawa

Gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya amince da korar masu taimaka masa na musamman guda 19 daga aiki.

A cewar wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar a yau Laraba, wannan ne zagayen farko na masu muƙamana siyasa da za a kora a yunƙurin da gwamnan ke yi na rage yawan ma’aikatan gwamnati.

Daga cikin waɗanda aka kora akwai mataimakin shugaban ma’aikatan gidan gwamnati da babban darakta a hukumar Public Procurement Authority.

Gwamna El-Rufai ya sha suka game da korar ma’aikata kusan 7,000 da ya yi, abin da ya jawo yajin aikin ma’aikata na kwana huɗu a jihar.

Sai dai gwamnatin na kare matakin da cewa tana kashe kusan kashi 80 cikin 100 na kuɗin da take samu wajen biyan albashi.

95 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...