Faduwar Tankar Mai Tayi Sanadiyar Jikkata Mutane 72 a Kano

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

Akalla Mutane 72 ne suka samu raunuka daban-daban a wata gobara da ta tashi da Maraice ranar Asabar din nan a gidan Man Fetur na Al-ihsan dake Sharada Phase 1, a Karamar Hukumar birni da Kewaye.


 Da yake ganawa da Jaridar News Watch Babban Sakatare, Kungiyar Red Cross ta Najeriya, reshen Jihar Kano Alhaji Musa D Abdullahi ya ce lamarin ya faru ne lokacin da wata tankar dakon Man Fetur ta kama da wuta.


 Ya ce kungiyar agajin gaggawa ta Red Cross ba tare da bata lokaci ba ta kwashe wadanda abin ya shafa 72 zuwa Asibitin Kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano don kula da lafiyarsu.
 ”Masu ba da agaji na Red Cross 7 sun halarci wajen Kuma sun Yi aikin sosai.


 “Lamarin ya rutsa da wasu ma’aikatan hukumar kashe gobara.”


 “Kamar yadda nake magana da ku yanzu wadanda abin ya shafa sun sami kulawar Ma’aikatan Lafiya”.

294 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...