Faduwar Tankar Mai Tayi Sanadiyar Jikkata Mutane 72 a Kano

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

Akalla Mutane 72 ne suka samu raunuka daban-daban a wata gobara da ta tashi da Maraice ranar Asabar din nan a gidan Man Fetur na Al-ihsan dake Sharada Phase 1, a Karamar Hukumar birni da Kewaye.


 Da yake ganawa da Jaridar News Watch Babban Sakatare, Kungiyar Red Cross ta Najeriya, reshen Jihar Kano Alhaji Musa D Abdullahi ya ce lamarin ya faru ne lokacin da wata tankar dakon Man Fetur ta kama da wuta.


 Ya ce kungiyar agajin gaggawa ta Red Cross ba tare da bata lokaci ba ta kwashe wadanda abin ya shafa 72 zuwa Asibitin Kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano don kula da lafiyarsu.
 ”Masu ba da agaji na Red Cross 7 sun halarci wajen Kuma sun Yi aikin sosai.


 “Lamarin ya rutsa da wasu ma’aikatan hukumar kashe gobara.”


 “Kamar yadda nake magana da ku yanzu wadanda abin ya shafa sun sami kulawar Ma’aikatan Lafiya”.

294 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...