Hukumar Hisbah a Kano ta Kori Jami’in ta da aka Kama da Matar Aure a Otel

Date:

Daga Jamila Sulaiman Aliyu

Hukumar Hisba ta jihar Kano ta Kori daya daga cikin manyan jami’anta, Sani Nasidi Uba, wanda aka fi sani da Sani Remo saboda haifar da abin kunya ga rundunar.”

Kwamitin da Kwamandan Janar, Ustaz Harun Muhammad Ibn Sina ya kafa, ya tuhumi Sani Rimo da samunsa da wani mummunan laifi.

Sani Rimo wanda aka san shi a sahun gaba wajen kamen karuwai da sauran ‘yan mata marasa gaskiya, an kama shi ne a cikin watan Faburairun bana tare da wata matar aure a wani dakin otal da ke yankin Sabon Gari a babban birnin jihar Kano.

Jami’in ya fadawa rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano cewa matar da ake magana a kai‘ yar dan uwansa ce wacce suke samun matsala da mijinta.

A cewarsa, ya ajiye ta a dakin otel har zuwa lokacin da za a warware matsalolin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...