Hukumar Hisbah a Kano ta Kori Jami’in ta da aka Kama da Matar Aure a Otel

Date:

Daga Jamila Sulaiman Aliyu

Hukumar Hisba ta jihar Kano ta Kori daya daga cikin manyan jami’anta, Sani Nasidi Uba, wanda aka fi sani da Sani Remo saboda haifar da abin kunya ga rundunar.”

Kwamitin da Kwamandan Janar, Ustaz Harun Muhammad Ibn Sina ya kafa, ya tuhumi Sani Rimo da samunsa da wani mummunan laifi.

Sani Rimo wanda aka san shi a sahun gaba wajen kamen karuwai da sauran ‘yan mata marasa gaskiya, an kama shi ne a cikin watan Faburairun bana tare da wata matar aure a wani dakin otal da ke yankin Sabon Gari a babban birnin jihar Kano.

Jami’in ya fadawa rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano cewa matar da ake magana a kai‘ yar dan uwansa ce wacce suke samun matsala da mijinta.

A cewarsa, ya ajiye ta a dakin otel har zuwa lokacin da za a warware matsalolin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gidauniyar Pyramid of Heart sun kai tallafin na’urar Oxygen Concentrated Asibitin Murtala dake Kano

Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhd dake Kano ya yabawa...

Da dumi-dumi: ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) ta dakatar da...

Ba mu da wata matsala da Ofishin mataimakin shugaban Kasa – NAHCON

Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ta karyata wani rahoto...

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...