Hukumar Hisbah a Kano ta Kori Jami’in ta da aka Kama da Matar Aure a Otel

Date:

Daga Jamila Sulaiman Aliyu

Hukumar Hisba ta jihar Kano ta Kori daya daga cikin manyan jami’anta, Sani Nasidi Uba, wanda aka fi sani da Sani Remo saboda haifar da abin kunya ga rundunar.”

Kwamitin da Kwamandan Janar, Ustaz Harun Muhammad Ibn Sina ya kafa, ya tuhumi Sani Rimo da samunsa da wani mummunan laifi.

Sani Rimo wanda aka san shi a sahun gaba wajen kamen karuwai da sauran ‘yan mata marasa gaskiya, an kama shi ne a cikin watan Faburairun bana tare da wata matar aure a wani dakin otal da ke yankin Sabon Gari a babban birnin jihar Kano.

Jami’in ya fadawa rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano cewa matar da ake magana a kai‘ yar dan uwansa ce wacce suke samun matsala da mijinta.

A cewarsa, ya ajiye ta a dakin otel har zuwa lokacin da za a warware matsalolin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...

Tinubu zai mayar da Fubara kan kujera gwamnan Rivers amma ya gindaya masa sharadi- Rahoto

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da mayar...

Yadda Makarantar JSS Unguwa uku dake K/H Tarauni ta Zama mafakar shaye-shaye da yan daba

Daga Mubina Ahmad Galadanchi Wasu daga cikin al'ummar unguwar unguwa...