Za a ci tarar Naira N100,000 kan duk wanda ya sare bishiya a Abuja

Date:

Hukumar Babban Birnin Tarayya Abuja ta ce daga yanzu duk wanda aka samu da laifin sare bishiya zai biya tarar N100,000.

Hukumar ta bayyana haka ne a sakon da ta wallafa a shafinta na Twitter ranar Litinin.

Sanarwar ta ambato Daraktar kula da wuraren shakatawa, Mrs Riskatu Abdulazeez, tana kara da cewa “haramun ne sare bishiyoyin da aka dasa a cikin gidajen jama’a ba tare da neman izinin gwamnati ba.”

A cewarta sare bishiyoyin na ta’azzara matsalolin da ke da dangantaka da sauyin yanayi don haka ba za su bari mazauna birnin su ci gaba da sare bishiyoyi ba tare da la’akari da illar yin hakan ba.

“Duk wanda ya sare bishiya ba bisa ka’ida ba zai biya tarar N100,000 kuma za a tilasta masa dasa sabbin bishiyoyi biyu domin maye gurbin wacce ya sare.” in ji Mrs Riskatu

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda kamfanin ganyen shayi na Z&Y ke fuskantar matsin lamba daga TOP TEAA

Wani matashin ɗan kasuwa daga jihar Kano, mai suna...

Gwamnatin Kano ta bayyana sunayen unguwannin da aka sami gurbatacciyar Iska

    Wani rahoto na mako-mako kan yanayin lafiyar iska da...

Sallah: Gwamnatin Kano za ta hukunta gidan wasan da ya bar masu shigar banza da shaye-shaye

Daga Rahama Umar Kwaru   A kokarin ta na yaki da...

Sallah: Hussari ya sauke kabakin arziki ga yan jam’iyyar APC na karamar hukumar Gwale

Daga Ibrahim Abubakar Diso   Tsohon Dan Majalisar wakilai da ya...