MatsalarTsaro :Gwamnatin jihar Kano ta bada Umarnin rufe Kwalejin Fasaha ta Bagauda

Date:

 Daga Nasiba Rabi’u Yusuf


 Gwamnatin jihar Kano ta bada umarnin rufe Kwalejin Fasaha ta Bagauda ba tare da bata lokaci ba.


  Kwamishinan Ilimi na jihar, Malam Muhammad Sanusi Sa’id Kiru ya sanar da cewa rufe kwalejin ya zama tilas biyo bayan wani rahoton tsaro da gwamnati ta samu da kuma bukatar kare rayukan dalibai, malamai da sauran ma’aikatan kwalejin.


 Cikin Wata sanarwa da Jami’in Hulda da jama’a na Ma’aikatar Ilimi Aliyu Yusuf ya aikowa Kadaura24 yace Kwamishinan ya bukaci iyaye da su hanzarta kwashe yaransu daga Kwalejin kuma su jira karin umarnin.


 Kwamishinan yayi amfani da damar don nuna godiyar gwamnatin jihar ga iyaye bisa goyan baya da hadin kai kan manufofi da umarnin gwamnati musamman kan al’amuran da suka shafi tsaro.

15 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...