Sallah: Ku Kwashe kayanku daga kan Hanya Don Gudun Cinkoso a Kasuwarmu-Shugaban Kofar Wambai

Date:

Daga Rabi’u Usman

Shugaban Kungiyar yan Kasuwar Kofar Wambai Alhaji Kabiru M Abubakar tsamiyar Mariri yayi Kira da Jan Hankali ga Kafatanin ‘yan Kasuwar Kofar Wambai dasu Kasance Masu Bin Doka da Oda Wajen Matsar da Kayan Su Daga Kan Hanya Kasancewar yanzu Lokaci ne na Cikar Kasuwanni Musamman lokacin da Jama’a Suke Zuwa Siyan Kayan Bukatar Sallah Karama da Muke Gab da Karkare Azumin Watan Ramadana Mai Albarka.

Kabiru yayi Kiran ne yayin da yake Ganawa da Manema Labarai a Wannan Rana, yana Mai Cewar, ta Haka ne Za’a Samu Damar Dakume Mutanen da Suke Shiga Kasuwanni da Zummar yin Siyayya daga Bisani Sai Su Bige da Satar Kayan Jama’a.

Ya Kara da cewa, tuni Sun Kafa Wani Kwamatin da Zai Dinga Zagayawa Domin Duba Halin da Kasuwar take Ciki da Kuma Wadanda Suka bi Umarnin da Kuma Hukunta Masu Kunnen Kashi da Dokar da Kasuwar ta Shimfida.

Sannan yace Sun Hada Kai da Jami’an tsaro na yan Sanda, Vigilantee, Karota, da Jami’an tsaro na Farin Kaya.

A Karshe dai Shugaban yayi Kira ga Al’umma Musamman Masu Mu’amalantar Kasuwar ta su dasu Kasance Masu Bin Dokokin da Shugabancin Kasuwar ta Sanya Su Kuma Kasancewar Masu Jin Tsohon Allah a Duk Al’amuran Su na Cinikayya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya...

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Sanarwa ta Musamman daga majalisar malaman Kano game da rasuwar Dantata

SANARWA MUHIMMIYA (GABATAR DA SALLATUL GA'IB) Assalamu Alaikum Warahmatullah, Sakamakon rasuwa...

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Iyalan marigayi Alhaji Aminu Alassan Dantata sun shaida cewa...