Daga Rabi’u Usman
Shugaban Kungiyar yan Kasuwar Kofar Wambai Alhaji Kabiru M Abubakar tsamiyar Mariri yayi Kira da Jan Hankali ga Kafatanin ‘yan Kasuwar Kofar Wambai dasu Kasance Masu Bin Doka da Oda Wajen Matsar da Kayan Su Daga Kan Hanya Kasancewar yanzu Lokaci ne na Cikar Kasuwanni Musamman lokacin da Jama’a Suke Zuwa Siyan Kayan Bukatar Sallah Karama da Muke Gab da Karkare Azumin Watan Ramadana Mai Albarka.
Kabiru yayi Kiran ne yayin da yake Ganawa da Manema Labarai a Wannan Rana, yana Mai Cewar, ta Haka ne Za’a Samu Damar Dakume Mutanen da Suke Shiga Kasuwanni da Zummar yin Siyayya daga Bisani Sai Su Bige da Satar Kayan Jama’a.
Ya Kara da cewa, tuni Sun Kafa Wani Kwamatin da Zai Dinga Zagayawa Domin Duba Halin da Kasuwar take Ciki da Kuma Wadanda Suka bi Umarnin da Kuma Hukunta Masu Kunnen Kashi da Dokar da Kasuwar ta Shimfida.
Sannan yace Sun Hada Kai da Jami’an tsaro na yan Sanda, Vigilantee, Karota, da Jami’an tsaro na Farin Kaya.
A Karshe dai Shugaban yayi Kira ga Al’umma Musamman Masu Mu’amalantar Kasuwar ta su dasu Kasance Masu Bin Dokokin da Shugabancin Kasuwar ta Sanya Su Kuma Kasancewar Masu Jin Tsohon Allah a Duk Al’amuran Su na Cinikayya.