Tambuwal yafi kowanne Gwamna aiki a Arewacin Nigeria – Obasanjo

Date:

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana, Rt. Hon. Aminu Waziri Tambuwal, a matsayin shugaba mai hangen nesa da kawo gyara a al’umma.

Jaridar The Nation ta ce tsohon shugaban na Najeriya ya bayyana haka ne a lokacin da ya kafa tubulin ginin wata katafariyar gadar sama da za ayi garin Sokoto.

Za a kashe Naira biliyan 3.4 kafin a kammala aikin wannan babbar gada sama mai hanyoyi tara.

Cif Olusegun Obasanjo ya yabi aikin da Mai girma Aminu Tambuwal yake yi musamman a harkar gina abubuwan more-rayuwa da inganta rayuwar marasa hali.

“Duk da matsalar da ake ciki yanzu na matsin tattalin arziki da rashin tsaro, ga tasirin annobar COVID-19, duk da karancin kudin-shiga, Tambuwal aiki ya ke yi.”

Ya ce: “Ina nan a baka ta cewa gwamna ne wanda ya ke aiki a jiharsa, ba a jiharsa kurum ba, daukacin Arewa maso yamma, musamman a bangaren kawo tsaro.”

“Ya na yin kokarin gaske, har a cikin abokan aikinsa da jam’iyyarsa, ya yi fice.” Inji Obasanjo.

A cewar Obasanjo, gwamnan na Sokoto ‘dan siyasa ne wanda yake kaunar jama’a daga ko ina. Obasanjo ya ce ya ji dadin gane wa kansa irin aikin da gwamnan yake yi.

120 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya bijiro da harajin da zai sa farashin man fetur ya karu

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ƙaddamar...

Sabbin Nau’o’in cutar Shan Inna 4 sun bulla a Kano

Hukumar kula da lafiya a matakin farko ta jihar...

NDLEA ‘Yan Sanda da Gwamnatin Kebbi Sun Karyata Jita-jitar Samar da Filin Jirgin Sama na Boye a jihar

  Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta...

Kotu a Kano ta kawo karshen Shari’ar wata Tunkiya

Daga Dantala Uba Nuhu, Kura An kawo ƙarshen shari’ar wata...