Mutanen gari sun kama ’yan bindiga a Zariya

Date:


Mutanen gari sun yi kukan kura sun cafke masu garkuwa da mutane da suka kai hari a unguwar Low Cost da ke Zariya.

A halin yanzu, wasu daga cikin ’yan bindigar suna hannun ’yan sanda bayan da mutanen unguwar suka yi musu kofar rago ranar Lahadi da tsakar dare.


Duk da haka, masu garkuwar sun tafi da matan aure biyu daga gidaje daban-daban, amma sun sako kananan yara biyun da suka dauka da tare da daya daga cikin matan, sai dai ba su sako mahaifiyar yaran ba.

Majiyarmu a Zariya ta ce ’yan bindigar sun harbi kananan yara almajirai guda hudu a lokacin farmakin da suka kai.

Daily Trust ta gana da almajiran da raunukan harin a jikinsu, kuma a halin yanzu suna samun kulawa a asibitin New City da ke a Zariyan.

74 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...