Mutanen gari sun kama ’yan bindiga a Zariya

Date:


Mutanen gari sun yi kukan kura sun cafke masu garkuwa da mutane da suka kai hari a unguwar Low Cost da ke Zariya.

A halin yanzu, wasu daga cikin ’yan bindigar suna hannun ’yan sanda bayan da mutanen unguwar suka yi musu kofar rago ranar Lahadi da tsakar dare.


Duk da haka, masu garkuwar sun tafi da matan aure biyu daga gidaje daban-daban, amma sun sako kananan yara biyun da suka dauka da tare da daya daga cikin matan, sai dai ba su sako mahaifiyar yaran ba.

Majiyarmu a Zariya ta ce ’yan bindigar sun harbi kananan yara almajirai guda hudu a lokacin farmakin da suka kai.

Daily Trust ta gana da almajiran da raunukan harin a jikinsu, kuma a halin yanzu suna samun kulawa a asibitin New City da ke a Zariyan.

74 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

‎Kawu Sumaila ya binciko kudaden da gwamnatin tarayya ta turawa kananan hukumomin Kano

‎ ‎Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Suleiman Abdulrahman Kawu...

Kamata ya yi wajen Mauludi ya Zama waje Mai nutsuwa saboda ana ambaton Allah da Manzonsa – Mal Ibrahim Khalil

Shugaban Majalisar shuhurar Malamai ta jihar Kano Sheikh Malam...

Ra’ayi:‎Tsarin Kwankwasiyya ya dora Kano a gwadaben cigaba a mulkin Gwamna Abba Kabir -Adamu Shehu Bello

‎ ‎Ra’ayi ‎ ‎Daga Adamu Shehu Bello (Bayero Chedi), Jigo a Kwankwasiyya...