Abdulmumini Kofa ya aika sakon ta’aziyyar Rasuwar Mahaifiyar Sarakunan Kano da Bichi

Date:

Daga Abubakar Y Abubakar

Babban Daraktan Hukumar Samar da gidaje ta Kasa Kuma Tsohon Dan Majalisar Kiru da Bebeji a zauren Majalisar Wakilai ta Kasa Hon. Abdulmumini Jibril Kofa ya aike da sakon ta’aziyyarsa ga Gwamnan jihar Kano Dr Abdullah Umar Ganduje da Sarakunan Kano da Bichi bisa Rasuwar Mahaifiyar Sarakunan Hajiya Maryam Ado Bayero ( Mai Babban Daki ).

Hon. Abdulmumini Jibril Kofa Wanda shi ne jagoran jam’iyyar APC na Kiru da Bebeji Kuma Jarman Bebeji ya bayyana rasuwar Mai Babban Daki a Matsayin babban Rashi ga al’ummar jihar Kano da Kasa baki Daya.

Jarman Bebejin yace labarin rasuwar Mai Babban Dakin ya girgiza shi sosai inda yayi Mata addu’ar samun Rahamar Allah madaukakin Sarki da Kuma fatan Allah ya gafarta Mata yasa aljanna ta zamo makoma a gareta.

“Ina Mika ta’aziyya ta ga Mai girma Gwamnan jihar Kano Dr Abdullah Umar Ganduje da Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero da Mai Martaba Sarkin Bichi Alhaji Nasiru Ado Bayero da al’ummar jihar Kano Dana Kasa baki Daya”. Inji Kofa

Abdulmumini Jibril Kofa yace Hajiya Maryam Ado Bayero uwace ta Gari data sadaukar da Rayuwar ta wajen baiwa ya’yanta tarbiyya ta gari wacce yanzu al’umma yanzu duk suke amfana.

68 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Sanarwa ta Musamman daga majalisar malaman Kano game da rasuwar Dantata

SANARWA MUHIMMIYA (GABATAR DA SALLATUL GA'IB) Assalamu Alaikum Warahmatullah, Sakamakon rasuwa...

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Iyalan marigayi Alhaji Aminu Alassan Dantata sun shaida cewa...

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...