Yan Bindiga suna son kure Hakuri na akan su – Shugaba Buhari

Date:

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya gargadi ‘yan bindigar da ke kashe-kashe musamman a arewacin kasar kan cewa “Su shiga hayyacinsu, su daina jin cewa gwamnati ba za ta iya maganinsu ba”.

Buhari ya yi wannan gargadin ne a ranar Alhamis yayin da yake Allah-wadai da kisan da ‘yan bindigar suka yi wa mutane sama da 50 a kauyukan Zamfara.

Shugaban wanda ya yi gargadin cewa “Za a kawo karshen Irin wannan rashin girmama rayuwar mutanen da ‘yan bindigar ke yi a kusa ba da dadewa ba”, ya kara da cewa, “Dole mu dakatar da wannan kisan da ake yi wa mutanen da ba su ji ba ba su gani ba”,

Shugaba Buhari ya tabbatarwa da al’ummar jihar Zamfara cewa “duk da gazawar da muka yi a kokarinmu na kare ‘yan kasarmu, ba za mu taba bayar da kai bori ya hau ba wajen murkushe wadannan marassa tausayin.”

Buhari ya yi alkawarin kaddamar da wani shirin soji na musamman a Zamfara domin “dakile hare-haren ‘yan bingidar” da kullum ke kamari.

“Gwamnatinmu ba za ta yarda da kai kashe ‘yan kauyen da ke talakawa ba suke fama da talauci da sauran matsalolin rayuwa,” in ji Buhari a wata sanarwa da kakainsa ya fitar Garba Shehu

71 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...